IQNA

Cibiyar Agaji Ta Musulmin Afirka Ta Kudu Ta Kai Taimako A Kasar Haiti

14:34 - February 02, 2022
Lambar Labari: 3486898
Tehran (IQNA) cibiyar bayar da agaji ta musulmin kasar Afirka ta kudu Gift of the Givers ta kai taimako ga al'ummar kasar Haiti.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, a cikin wannan makon ne ma'aikatan cibiyar agaji ta musulmin kasar Afirka ta kudu Gift of the Givers ta isa kasar Haiti domin kai taimako ga al'ummar kasar .

Rahoton ya ce wannan kugiya wadda musulmin kasar Afirka ta kudu masu hannu da shuni suka kafa, tana gudanar da ayyuka na jin kai a kasashen duniya da dama.

Daga cikin irin ayyukan da kungiyar ke gudanarwa har da gina makarantu a yankuna na marasa galihu, da kuam samar da madatsun ruwa, da gina kwalbati.

Baya ga haka kuam a bangaren ayyukan kiwon lafiya kungiyar tana guanar da ayyuka na samar da magunguna ga mabukata, da kuma gina dakunan shan magani.

Yanzu haka dai a kasar Haiti kungiyar tana gudanar da ayyuka na tallafawa jama'a a bangarori na kiwon lafiya da ilimi, da kuma samar da ruwan sha a wasu yankunan da suke fuskantar matsala a wannan bangare.

 

4032686

 

 

 

captcha