IQNA

Ci gaba da kai hare-hare da gwamnatin sahyoniyawan ke kaiwa Gaza bayan kawo karshen tsagaita wuta

16:32 - December 01, 2023
Lambar Labari: 3490235
Gaza (IQNA) A daidai lokacin da aka kawo karshen yarjejeniyar tsagaita bude wuta na jin kai a zirin Gaza, sojojin gwamnatin sahyoniyawan mamaya sun sake kai hare-hare a wannan yanki ta sama da kasa a safiyar yau. Sakamakon wadannan hare-haren Palasdinawa da dama sun yi shahada tare da jikkata.

Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Aljazeera cewa, yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka yi a zirin Gaza da aka kwashe tsawon kwanaki 7 ana yi ta kawo karshe da karfe 7 na safe agogon kasar a yau Juma’a.

Ofishin yada labarai na jihar Gaza ya sanar da cewa, jiragen saman mamaya sun kai hare-hare a kudancin zirin Gaza. Kazalika, majiyoyin cikin gida sun sanar da cewa 'yan mamaya sun kai hari a yankunan Sheikh Rezwan da kuma arewacin birnin Gaza.

A hukumance sojojin yahudawan sahyoniya sun sanar da sake komawa fada da kungiyar Hamas a zirin Gaza. Avikhay Adrei kakakin sojojin gwamnatin sahyoniyawan ya yi ikirarin cewa: Hamas ta karya yarjejeniyar tare da harba harsasai kan Isra'ila.

Ya ce: Sojojin Isra'ila sun sanar da sake kunna wuta a arangamar da suka yi da Hamas.

Adrei ya kara da cewa: Bibiyan kunna siren gargadi a Kibbutz Havlit ya nuna cewa an harba rokoki da dama daga zirin Gaza zuwa Isra'ila, wadanda aka kama.

 

 

4185109

 

captcha