IQNA

Jiragen Yakin Isra'ila Sun Kai Hari A Gaza

21:43 - November 02, 2019
Lambar Labari: 3484216
Bangaren kasa da kasa, sojojin Isra'ila sun kai hari a Zirin Gaza inda suka kashe bafalastine guda da jikkata wasu.

Rahotanni da ke fitowa daga yankin palasdinu sun bayyana cewa jiragen yakin Isra'ila sun yi lugudan wutakan wasu wuraren kungiyar gwagwarmaya ta hamas aKhan yunusda wasu yankuna a zirin gaza kuma yayi sanadiyar shahadar mutum daya, sao’ibayan da sojojin Isra'ila sun jikkata gomomin palasdinawa a lokacin da suke gudanar da zanga zanga a yakin gabar teku .

Kamfanin dillancin labaran iqna, wata sanarwa da jami’an soji Isra'ila suka fitar sun nuna cewa harin na jiya sun kai shi ne a matsayin mayar da martani game da makaman roka 10 da aka harba su zuwa Israila daga yankin zirin gaza

A gafe guda ma sojojin Isra'ila sun bude wuta kan wasu palasdinawa masunta a Arewacin yankin Gaza, bayan jikkata palasdinawa da dama a ya yin gudanar da zanga zangar neman hakkin palasdinawa yan gudun hijira su koma gida.

A wani rahoto da ma’aikatar kiwon lafiya ta Yankin Gaza ta fitar ya nuna cewa: wani bapalasdine guda ne ya yi shahada ya yin da wasu casain da shida kuma suka samu raunuka sakamakon taho mu gaba da aka yi da sojojin Isra'ila a ya yin zanga –zangar ta jiya juma’a.

3853888

 

 

captcha