Kakakin harkar musulunci Malam Ibrahim Musa ya bayyana cewa za su kalu balance wannan hukunci ta hanyar doka a kotu.
Gwamnatin jahar kaduna ta dauki wanan matakin ne dai a daidai lokacin da ake shirin gudana da tarukan Ashura na Imam Hussain (AS) wanda shi ne taro mafi girma da mabiya harkar musulunci suke gudanarwa a Zaria a kowace shekara.
Babban dalilin da gwamnatin ta bayar da shi ne mabiya harkar muslunci suna taka doka tare da tare hanyoyi a lokacin tarukansu, kamar yadda kuma tace ta yi hakan ne bayan da kwamitin bincike da ta kafa ya bukaci a haramta kungiyar.
Sai a nata bangaren harkar muslunci ta karyata dukkanin abubuwa da aka fada a matsayin hujja, tare da bayyana cewa akwai abin da shi kansa kwamitin ya abta wand aba a yi maganarsa ba, shi ne kisan mutane akalla 348 da aka bizne sua cikin rami guda a Kaduna, tare da yin kira da ahukunta sojoji da suka aikata hakan, amma gwamnatin Kaduna ba ta ambaci wannan ba.
Yanzu haka dai jagoran harkar musluncia Najeriya Sheikh Ibrahim Zakzaky yana tsarea ahannun mahukunta ba tare da gurfanar da shia gaban kuliya ba, duk kuwa da cewa rahotanni sun tabbatar da cewa yanayin lafiyarsa na ci gaba da kara tabarbarewa, musamman ma idonsa guda da sojoji suka harba da bindiga wanda ya daina aiki, sai kuma gudan da ya rage yanzu ya fara samun matsala.