Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na kasar Bahrain cewa, al’ummar yankunan Sanab da Aali na kasar Bahrain sun gudanar da zanga-zangar nuna adawa da manufofin gwamnatin Khalifa na daidaita alaka da gwamnatin sahyoniyawan, inda suka bayyana goyon bayansu ga fursunonin da ke gidan yarin Khaliifa tare da sabunta mubaya’arsu ga Ayatullah Issa Qasim.